Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya na kan tafiya ketare zuwa kasar Kenya inda daga nan zai wuce London don neman magani.
Sanarwa daga ofishin shugaban na baiyana cewa shugaban zai yi ziyarar aiki ta kwana 3 a Kenya inda daga nan zai wuce London da zai kai mako biyu a can.
Shugaban kan je London don duba lafiyar sa tun kafin lashe zaben s a shekara ta 2015.
Cutar da a ka shaida ta fi damun shugaban ita ce ciwon kunne, amma wani lokaci da ya dade a London gabanin zaben sa na farko ya ba da shawarar a guji amfani da magani ba tare da izinin likita don hakan kan kawo illa da ta kan kara cuta maimakon samun waraka.
KU KASANCE DA NOBLEN DON SAMUN INGANTATTUN LABARAI A KOWANE LOKACI😀😀😀