Wasu rokoki uku sun yi dirar mikiya kan cibiyar sojan saman Iraki dake daf da birnin Bagadaza inda ‘yan kwangilar Amurka ke zama.
A cibiyar a ke adane da jirgin yaki kirar F-16 da Iraki ta sayo daga Amurka da kuma ‘yan kwangilar ke kula da su.
Helkwatar tsaron Amurka Pentagon ta ce ba wanda ya samu rauni a sanadiyyar harin.
Kimanin rokoki 30 ne a ka harba kan muradun Amurka a Iraki tun hawan sabon shugaban Amurka Joe Biden.
Amurka kan aza laifin irin wannam hari kan kungiyoyin aware na Iraki da Iran ke marawa baya.
In za a tuna Amurka a zamanin mulkin tsohon shugaba Donald Trump ta kai farmaki a filin saukar jiragen sama na Bagadaza inda ta hallaka babban kwamandan kasar Iran Kassim Soulaimani da hakan ya jawo bakin cikin ainun daga hukumomin Iran mabiya darikar shia.
I do not even know how I ended up here, but I thought this post was
great. I do not know who you are but certainly you are going to a famous blogger if you aren’t
already 😉 Cheers!
SAVE BIG ON GASOLINE AT THE PUMP >>> http://coolralph.com
You ought to take part in a contest for one of the highest quality websites
on the web. I most certainly will recommend this website!