Mai Kaltungo a jihar Gombe ya bukaci gwamnatin Najeriya ta tantance allurar rigakafin korona kafin fara amfani da ita kan jama’a.
Basaraken da ke magana a liyafa ga manema labaru, ya ce zai yi kyau gwamnatin ta gaiyaci masana kimiyyar magunguna su nazarci magungunan na rigakafin don hakan zai sanya hankalin mutane su kwanta.
Najeriya na shirin kashe Naira biliyan 400 don odar alluran rigakafin da za a yi wa kashi 70% na jama’ar kasar allurar rigakafin.
KU KASANCE DA NOBLEN DON SAMUN INGANTATTUN LABARAI A KOWANE LOKACI😀😀😀