Shugaban kungiyar makiyaya ta Miyetti Allah a karamar hukuamr Jama’a a jihar Kaduna Alhaji Bayero Babiyo ya ce su na yin duk abu mai yiwuwa don karfafa zaman lafiya a yankin Kaduna ta kudu.
Bayero Babiyo ya ce su kan zama da manoma don samar da fahimtar juna.
Duk da haka Babiyo ya koka cewa wasu bata gari kan sa guba a cikin lemo inda shanu kan ci su mutu nan take.
Babiyo ya bukaci hukumomi su bincika kalubalen don magance shi.
Hakanan ya bukaci dawo da burtali da ya ke yankin tun zamanin turawa.
Babiyo ya ce duk bayanan taswirar yankin noma da kiwo na nan a hannun gwamnati.
KU KASANCE DA NOBLEN DON SAMUN INGANTATTUN LABARAI A KOWANE LOKACI😀😀😀
Hi there! This post couldn’t be written any better! Reading through this post reminds me of my previous room mate! He always kept talking about this. I will forward this article to him. Pretty sure he will have a good read. Thank you for sharing!