Masu satar mutane da su ka shigo da manyan bindigogi gidan shugaban APC na jihar Nassarawa Philip Shekwpor, sun kashe shi daga bisani da yar da gawar sa kusa da gidan sa a Lafiya babban birnin jihar.
Tun farko barayin sun bude wuta da hakan ya sanya masu gadin gidan neman wajen tsira, inda su ka balle kyauren gidan daga nan su ka shiga dakin marigayin su ka fito da shi inda bayan wani lokaci a ka samu gawar sa.
Da farkon labarin kakakin rundunar ‘yan sanda a jihar Ramhan Nandel ya tabbatar da sace Shekwpor da baiyana azamar jami’an na ceto shi ba tare da samun kwarzane ba.
Nassarawa na daga jihohin da matsaar satar mutane ta ta’azzara.
KU KASANCE DA NOBLEN DON SAMUN INGANTATTUN LABARAI A KOWANE LOKACI😀😀😀
I am in fact thankful to the holder of this site who has shared this impressive post at here.
Hi my loved one! I wish to say that this post is amazing, nice written and come with almost all important infos.
I would like to see extra posts like this .