Kotu a Ikeja Lagos za ta yanke hukunci kan gagarumin barawon mutanen nan Evans ranar 25 ga watan Febrerun badi.
In za a tuna tsohon jami’in aiki da cikawa na ‘yan sanda Abba Kyari ya cafke Evans da gurfanar da shi gaban kotu.
A na tuhumar Evans da sauran abokan satar sa da su ka hada da
Okwuchukwu Nwachukwu, Ogechi Uchechukwu, Chilaka Ifeanyi, Victor Aduba da Uche Amadi.
Lauyan Evans mai suna Victor Opara bukaci babbar kotun ta jihar Lagos ta sake Evans, ya na mai cewa wai ba a same shi da laifin da a ke zargin sa da shi kai tsaye ba.
Bai zama abun mamaki ba yanda sauran wadanda a ke tuhuma su ka cewa kotun ba su aikata tuhumar biyu da a ke yi mu su ba.
Tuhumar ta hada da sace mutane da hada baki wajen sace mutane don karbar kudin fansa.
KOTU ZA TA YANKE HUKUNCI KAN BARAWON MUTANEN NAN EVANS A WATAN FEBRERUN BADI

KU KASANCE DA NOBLEN DON SAMUN INGANTATTUN LABARAI A KOWANE LOKACI😀😀😀
I know this if off topic but I’m looking into starting my own weblog and was curious what all is required to get set up? I’m assuming having a blog like yours would cost a pretty penny? I’m not very web smart so I’m not 100 positive. Any recommendations or advice would be greatly appreciated. Appreciate it
Hello! Would you mind if I share your blog with my facebook group? There’s a lot of people that I think would really appreciate your content. Please let me know. Thanks