Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci ‘yan jam’iyyar sa su dage don kar PDP ta dawo mulki a 2033.
Shugaban wanda ke jawabi a taron fidda gwani na APC, ya nuna fargaba in PDP ta dawo za ta maysr da hannun agogo baya a nssarorin da ya ce ya cimma.
Muhammadu Buhari ya ce hakan zai yiwu ne da zabar dan takara da zai samu karbuwa.
Hakanan shugaban ya bukaci duk wanda ya samu nasara ya kyautatawa wadanda su ka janye ma sa.
Shugaban wanda ya fice kafin kada kammala kada kuri’a, ya hori jagororin jam’iyyar su rungumi hanyar sasantawa.
KU KASANCE DA NOBLEN DON SAMUN INGANTATTUN LABARAI A KOWANE LOKACI😀😀😀