Helkwatar tsaron Najeriya ta ce ta na labarin cewa duk daliban makarantar sakadandaren Kanakara a jihar Katsina da masu satar mutane su ka dauke na nan lafiya hannun wadanda su ka sace su.
Kakakin runduna tsaron Manjo Janar John Enenche ya ce daga labarun da su ka tattara daga jami’an tsaro da gwamnatin Katsina na nuna duk yaran su na nan lafiya a hannun miyagun irin.
Enenche ya ce sojoji ba su da tsarin tattaunawa da ‘yan ta’adda don haka ba sa cikin masu tuntubar barayin don karbo yaran.
Duk da haka Enenche ya ce soja za su cigaba da aikin su na tsaro don karbo yaran lami lafiya.
KU KASANCE DA NOBLEN DON SAMUN INGANTATTUN LABARAI A KOWANE LOKACI😀😀😀
Thank you for the auspicious writeup. It in fact was a amusement account it.
Look advanced to more added agreeable from you! By the way, how could we communicate?