Kakakin kamfen din PDP a taraiya Buba Galdima ya yabawa Amurka da cewa barazanar da ta yi ta hana masu magudin zabe shiga kasar ta, ta sanya masu nufin magudin su ka samu sanyin guiwa. Galadima wanda har yau bai aiyana ya bar APC ba amma PDP ya ke yi wa aiki tun a babban zaben 2019 bayan yunkurin kafa bangare a APC da ya yi bai yi tasiri ba. Dan siyasar wanda a baya shi ne kan gaba a marawa shugaba Buhari baya gabanin zaben 2015, ya nuna fatar jami’an tsaro da sauran ma’abota zabe za su bi sahu wajen yin adalci don karfafa turbar dimokradiyya.
KU KASANCE DA NOBLEN DON SAMUN INGANTATTUN LABARAI A KOWANE LOKACI😀😀😀
I am really inspired along with your writing abilities as smartly as
with the layout to your blog. Is this a paid theme
or did you modify it your self? Anyway keep up the nice quality writing, it’s rare to look a nice blog like this
one these days..