Zaben Kananan Hukumomi A Katsina; APC Ta Lashe Kananan Hukumomi 31,An Soke Na Dutsinma

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Katsina ta bayyana sakamakon zaben shugabannin kananan hukumomi da na kansiloli da aka guudanar a kananan hukumomi 31 daga cikin 34 na jihar

Sakataren hukumar zaben Lawal Hassan Faskari ne ya bayyana sakamakon zaben a shelkwatar hukumar dake birnin Katsina

Kamar yadda ya bayyana Jam’iyyun siyasa goma sha biyu ne suka fafata a zaben inda jam’iyyar APC ta samu nasara a kananan hukumomi 31 da aka kammala, yayin da ake jiran sakamakon kananan hukumomin Funtua da Daura,inda kuma aka soke na karamar hukumar Dutsinma

Lawal Faskari ya kara da cewa a dukkanin kananan hukumomin wadanda Jam’iyyar ta APC ta lashe zaben ta kuma samu nasarar dukkanin kansilolin da aka kammala zaben su

Ya bayyana zaben a matsayin wanda ya gudana cikin lumana da kwanciyar hankali tare da yabama dukkanin masu ruwa da tsaki da suka bada gudummuwa wajen samun nasarar zaben a fadin jihar

Sai dai,sakataren hukumar ya bayyana cewa an soke zaben karamar hukumar Dutsinma biyo bayan fuskantar wasu matsaloli yayin gudanar da zaben

Yana mai cewa ana jiran isowar sakamakon na kananan hukumomin Daura da Funtua a lokacin da ake bayyana sakamakon

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *