‘Yan wasan kasar Iran sun yi nasarar lashe lambar zinare a wasan Nahiyar Asia

Shugaban hukumar kula da harkokin wasanni da matasa ta Bandar Torkaman, ya bayyana cewa, lambar zinare ta gasar wasannin tekun Asiya da kasar  Thailand ta karbi bakuncinsa. A bangaren kayak na mutum 2,  Adel Mojallali, daya daga cikin ‘yan wasan Olympics na birnin Bandar Torkman, ya sami nasara.

Abdulqadir Onagh ya ce, a wannan gasa, tawagar wasan kwale-kwale ta Iran mai mutane biyu, Adel Mojallali da Shaho Naseri sun zo a matsayi na farko na Nahiyar Asiya, inda suka samu lambar zinare. A wannan gasa da aka gudanar a Thailand, ‘yan wasa daga Kazakhstan, Uzbekistan, Indonesia da Thailand sun zo a matsayi na gaba, in ji shi.

Birnin Bandar Torkaman mai yawan jama’a 80,000 yana yammacin lardin Golestan da kuma bakin tekun Gorgan Gulf kuma yana da ‘yan wasa da dama.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *