Kotun daukaka kara dake zamanta a Sokoto, ta tabbatar da daurin shekaru 14 a gidan yari da aka yanke wa mataimakin daraktan hukumar FCC, Alhaji Ahmed Balarabe, da laifin damfarar wasu masu neman aikin kudi har naira miliyan takwas (N8m). babbar kotun jihar Zamfara.
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta (ICPC) ta gurfanar da Balarabe a gaban mai shari’a Bello Shinkafi na babbar kotun jihar Zamfara kan tuhume-tuhume biyu na samun kudi ta hanyar karya.
ICPC ta sanar da kotun yadda Balarabe a lokacin da yake rike da mukamin Kodinetan FCC a jihohin Zamfara da Sokoto a tsakanin shekarar 2017 zuwa 2018 ya karbi sama da Naira miliyan 8 daga hannun masu neman aikin da ba su ji ba, tare da alkawarin ba su ayyukan yi, wanda hakan ya saba wa sashe na 1 (1)(a) na Advance Fee Fraud Act 2006.
A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Shinkafi ya yanke wa Balarabe hukuncin daurin shekaru 14 a gidan yari tare da zabin tarar N500,000. Kotun ta kuma yanke hukuncin cewa wanda ake tuhuma ya biya Naira miliyan 7 ga wadanda aka samu da laifin.
Sai dai wanda ake tuhumar bai gamsu da hukuncin ba, ya garzaya kotun daukaka kara domin soke hukuncin da kotun ta yanke.
Sai dai a wata sanarwa da kakakin ICPC, Azuka Ogugua ya fitar a ranar Talata, ya ce; “Yayin da lauyan sa (Balarabe), Mista A. Y. Abubakar ya ce ya kamata kotu ta yi watsi da hukuncin, lauyan ICPC, Mashkur Salisu, ya mika hukuncin ya yi daidai da tanade-tanaden dokar cin hanci da rashawa na shekarar 2006 da wanda ake tuhuma ya karya.
Sanarwar ta ci gaba da cewa; “Bayan sauraron gardama daga lauyoyin biyu, kotun gaba daya ta yi watsi da karar bisa dalilan rashin cancanta sannan ta tabbatar da hukuncin da kotun ta yanke.”