Hukumar makaranta ta mika shugabanci ga dalibanta

 

Wata Makarantar al’umma mai suna “Gafai Community Secondary School,  a ranar Litinin da  ta mika shugabancin makarantar na kwana daya ga wasu zakarun dalibanta da suka zamo fitattau a fagen  darussan da makarantar ke koyarwa.  

Makarantar , ta mika  shugabancin gudaran da makarantar ga daliban, ta yadda suka gabatar da duk ayyukan makarantar a tsawon yini kamar yadda shugabannin makarantar ke aiwatarwa.

A yayin tattaunawa da majiyarmu, shugabannin makarantar na  Gafai Community Secondary School, sun bayyana dalilin yi ma wadannan daliban wannan karramawa a matsayin tagomashi a gare su saboda kwazon da suka nuna.

Muttaka Abdullahi, shugaban bangaren  karamar makarantar (junior) ya bayyana cewa, “Dalilin da ya sa yin wannan shi ne domin kara jawo hankalin yara su kara maida hankali, su kara kwazo ga karatunsu.” 

 Shi ma Naziru Sani  Shugaban bangaren babbar makarantar ya ce ,”Mun yi hakan ne don daliban su kara himmatuwa ga karatusu, domin su zama cikakkun mutane masu inganci,  a fannin ilimi, kuma domin sauran dalibai su yi koyi da su.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *