Yunkurin juyin mulki a Guinea Bissau?

A wannan Talata ne aka rika jin karar harbe-harben bindigogi a babban birnin Guinea Bissau.
Rahotannin daga kasar sun bayyana cewa, wasu mutane dauke da makamai sun zagaye fadar shugaban kasa.
Ana kyautata zaton shugaban kasar Umaro Dissoco Embalo, da Firaminista Nuno  Gomes Nabiam suna wajen taron majalisar  ministocin kasar.
Fadar gwamnatin Guinea Bissau  tana kusa da filin saukar jiragen sama na kasar. 
maharan na tsare da wasu jami’an gwamnatin kasar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *