Shugaban Jam’iyyar PDP Iyorchia Ayu ya dawo daga tattakin da ya yi Kasar Turai.

Shugaban Jam’iyyar PDP Iyorchia Ayu ya dawo daga tattakin da ya yi Kasar Turai.

Shugaban Jam’iyyar PDP Iyorchia Ayu ya dawo gida Nijeriya bayan kwashe makonni biyun da ya yi a Kasar Turai.
Mai Shugaban shawara a harkokin yada Labarai Mista Simon Imobo Tswam ya bayyana hakan a wata sanarwar da ya rabawa manema Labarai ranar Juma’a a Abuja.
Yace Ayu, wanda ya bar kasar nan ranar 14 ga watan Satumba ya sauka Abuja ta Filin jiragen saman kasa da kasa na Nnamdi Azikwe da misalin karfe 7:00 na dare.
Idan za a iya tunawa, Iyorchia Ayu ya mika ragamar tafiyar da Jam’iyyar ga Naibinsa dake kula da Shiyyar Arewa Ambasada Iliya Damagun sannan ya sanar da hakan ga Hukumar INEC.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *