Jinin yarinyar da aka kashe ba zaya tafi a banza ba- Ganduje

Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya ba da tabbacin cewa, jinin yarinya ’yar shekaru 5 Hanifa da malamin makarantar su Abdulmalik Tanko ya yi wa kisan gilla, ba zaya  tafi  a banza ba.
A matakin farko,  gwamnatin ta rufe makarantar da wancan  malamin ke jagoranta, wato NOBLE KIDS don gudanar bincike.
Kwamishinan yada labaru na jihar Kano  Muhammad Garba, ya ba da sanarwar cewa,  tabbas gwamnti za ta tabbatar  da an hukunta wanda ya yi kisan.
Malamin Abdulmalik Tanko wanda ya sace Hanifa, ya karbi kudin fansa, sannan ya kashe ta, ta hanyar sanya ma ta guba, ya na hannun ‘yan sanda inda bayan kammala bincike za a gurfanar da shi gaban kotu tare da wadanda suka aikata wannan  mugun aiki.
Kisan gillar  Hanifa, ya jawo matukar takaici da bacin rai tsakanin dukkan ‘yan Najeriya inda a ka yi ta yada hotunanta  da mika ta’aziyya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *