ZABEN 3023: TINUBU YAYI FARAR DABARA_Cewar Gwamna Zulum

Gwamnan Jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya bayyana zaben Senata Kashim Shatima da Dan takarar Jam’iyar APC Bola Tinubu yayi da cewa shine dabara.
Shidai Bola Tinubu a ranar Lahadi ya bayyana Kashim Shettima a matsayin Wanda zai ma shi mataimaki.
Shettima dai shine sanata mai wakilta Borno ta tsakiya bayan ya gama wa’adin shi na Gwamna a shekarar 2019.
Zulum ya bayyana Sanata Kashim a matsayin kwararren Dan siyasa mai hasashe da basira.
Yace zaben nashi kamar ni akai mawa, inda zan goya mashi baya ba dare ba rana dan ganin an samu gaggarumar nasara.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *